Hukumar kula da Lafiya ta duniya ta bayyana wa'adin Covid19
Hukumar kula da lafiya ta duniya wacce aka fi sani da WHO(World Health Organization) a turance, ta bayyana wa'adin cutar sarkafewar numfashi ta coronavirus wato Covid19. Wani rahoto da gidan telebijin na Aljazeera ya fitar a yau 16/4/2020 ya bayyana cewa hukumar kula da lafiya ta duniya ta yi ikrarin cewa cutar annobar sarkafewar numfashi ta coronavirus wato Covid19 za ta iya kaiwa shekarar 2024 a fad'in duniya wanda hakan na nufin za ta iya kaiwa tsawon shekaru hud'u kafin a samar da ingantaccen maganinta da zai aiki a kan ta, don ba cuta ce irin sauran cututtuka ba, wannan cutar ta na barazana ne ga duniya gabad'ya dangane da tattalin arzuki lafiyar jam'a.
Rahoton Aljazeera
Rahoton Aljazeera
Comments
Post a Comment
Please leave your comment here